Ba kanta: Dan majalisar wata jiha a Najeriya yayi batan dabo

Ba kanta: Dan majalisar wata jiha a Najeriya yayi batan dabo

Labarin da muke samu da dumin sa na nuni ne da cewa kawo yanzu dai jami'an tsaron Najeriya ana kyautata zaton sune suka sace dan majalisar jihar Ekiti kuma shugaban marasa rinjaye a majalisar mai suna Honarable Gboyega Aribisogan.

Kamar dai yadda muka samu, an cewa da sanyin safiyar yau ne dai aka ce jami'an tsaron sun yi awon gaba dan majalisar inda kuma ake kyautata zaton sun tafi da shi a garin Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.

Ba kanta: Dan majalisar wata jiha a Najeriya yayi batan dabo
Ba kanta: Dan majalisar wata jiha a Najeriya yayi batan dabo

KU KARANTA: Ko me Buhari zai je yi Landan kuma?

Da yake karin haske game da lamarin, kanin dan majalisar mai suna Sola ne ya bayyana cewa wata tawagar jami'an 'yan sandan nan ta musamman dake hana manyan laifukan fashi da makami na musamman watau Special Anti Robbery Squad (SARS) da kuma 'yan sandan farin kaya ne suka tafi da shi.

A wani labarin kuma, Da alama dai rikicin dake a ta faruwa a tsakanin 'ya'yan jam'iyyar All Progressives Congress, APC mai mulki a Najeriya bai da alamun karewa musamman ma dai bisa dalilin wa'adin shugabannin jam'iyyar a dukkan matakai.

Wannan dai kamar yadda muka samu na faruwa ne biyo bayan kiran da daya daga jigogin jam'iyyar dake a jihar Bayelsa ta shiyyar kudu maso kudancin kasar mai suna Perekeme Kpodo da yayi na cewa ya kamata shugaban jam'iyyar na yanzu Cif Oyegun ya sauka daga kan mukamin sa cikin ruwan sanyi.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel