Tsautsayi da karar kwana: Allon talla ya kashe mutane 3 a Lagos

Tsautsayi da karar kwana: Allon talla ya kashe mutane 3 a Lagos

- Idan ajali yayi kira ko ba ciwa dole ace

- Kimanin mutane 3 ne suka bakunci lahira a sandiyyar fadowar babban allon talla

Wani babban allon sanarwa na girke, yayi sanadiyyara salwantar rayukan fasinjoji uku da kuma raunata akalla bakwai bayan da ya fado a kan wata motar fasinja. Lamarin dai ya faru ne, a tashar mota dake kan titin Oshodi zuwa Apapa na Jihar Lagos.

Tsautsayi da karar kwana: Allon talla ya kashe mutane 3 a Lagos
Tsautsayi da karar kwana: Allon talla ya kashe mutane 3 a Lagos

KU KARANTA: An gwabza kazamin fada tsakanin sojoji da tsageran daji a Zamfara

Da yake bayyana yadda abin ya afku, wani wanda allon ya fado a gaban idonsa, ya shaida cewa,

“Wata katuwar motar gine-gine ce dake aiki a kan babban titin Oshodin zuwa Apapa, ta daki allon tallan bisa kuskure, wanda faruwar hakan ke da wuya sai ya runtumo kan motar fasinjar.”

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Lagos, Adesina Tiamiyu, ya tabbatarwa da majiyar Premium Times faruwar al’amarin da yammacin yau.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko buƙatar bamu labari, tuntuɓe mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://facebook.com/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel