Atiku Abubakar yayi Allah wadai da kashe kakakin jam’iyyar PDP da aka yi

Atiku Abubakar yayi Allah wadai da kashe kakakin jam’iyyar PDP da aka yi

- Atiku yayi Allah wadai da kashe mai magana da yawun bakin jam’iyyar PDP na jihar Adamawa

- Atiku Abubakar ya mika ta'aziyar sa ga iyalan Sam Zadoch

Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar, yayi Allah wadai rikicin da ake yi a jihar Adamawa, wanda yayi sanadiyar mutuwar mai magana da yawun bakin jam’iyyar PDP na jihar Adamawa, Sam Zadock, da mutane 12.

A jawabin da Atiku Abubakar, ya fitar a ranar Laraba, yayi Allah wadai da rikicin addini da ya barke tsakanin Musulmai da Kristoci Kudancin jihar Kaduna a ranar Litinin wanda yayi sanadiyar asara rayuka da dukiyoyi a jihar.

Atiku Abubakar yayi Allah wadai da kashe kakakin jam’iyyar PDP da aka yi
Atiku Abubakar yayi Allah wadai da kashe kakakin jam’iyyar PDP da aka yi

Abubakar, ya nuna damuwar sa akan yadda kashe-kashe da tashin hankali ya zama ruwan dare a Najeriya.

KU KARANTA : Rikicin Adamawa : An kashe kakakin jam’iyyar PDP na jihar Adamwa - PDP

A ranar Laraba jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar, Mista Sam Zadoch ta sanadiyar rikici da ya barke tsakanin ‘yan tawayen kabilar Bachama da makiyaya a yankin Numan Demse a ranar Talata.

Atiku Abubakar ya mika ta’aziyar sag a iyalana Zadok da mutanen da rikicin ya shafa.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel