Wasu malamai biyu na addinin Kirista sun riga mu gidan gaskiya a wani mummunan hatsari na jihar Ondo

Wasu malamai biyu na addinin Kirista sun riga mu gidan gaskiya a wani mummunan hatsari na jihar Ondo

Rundunar 'yan sandan jihar Ondo ta cafke wani direban motar daukan kaya, Juwon Ariyibi, bisa laifin kisan mutane biyu da motarsa a garin Ipele na ƙaramar hukumar Owo ta jihar.

Kakakin hukumar, Mista Femi Joseph, shine tushen wannan rahoto da ya bayyana cewa, hatsarin ya afku ne a ranar Litinin din da gabata a yayin da wadanda suka riga mu gidan gaskiya, Fasto Oluwajuwon Adebayo da kuma Fasto Sunday Ajenifuja suke tafe a kan babur din su.

Legit.ng ta fahimci cewa, baya ga kasancewar su malaman addinin kirista sun kuma kasance malaman wata makarantar firamare ta gwamnati dake ƙaramar hukumar Akure ta Arewacin jihar, inda ajali ya yi musu halinsa a yayin da suke tafe a hanyarsu da zuwa wajen aiki.

Jami'an tsaro
Jami'an tsaro
Asali: Depositphotos

Rahotanni da sanadin jaridar The Punch sun bayyana cewa, an yi gaggawar miƙa wannan malamai biyu asibiti a yayin da hatsarin ya afku, wanda daga bisa ni suka ce ga garin ku nan.

KARANTA KUMA: Wani hamshaƙin ɗan kasuwa ya yi kuskuren kashe 'yar sa a jihar Imo

Kakakin hukumar ya ƙara da cewa, akwai tuƙin ganganci a ɓangaren direban babbar motar, kuma za miƙa shi kotu da zarar sun kammala bincike.

A na ta ɓangaren, shugabar cibiyar ilimi ta jihar Ondo, Misis Oladunni Odu ta bayyana rashin jin dadin ta dangane da wannan tsautsayi da ya afkawa malaman, inda kuma ta miƙa saƙon ta'aziyartar ga iyalan wadanda suka yi rashin.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntuɓe mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://facebook.com/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng