Dutse: Gobarar wuta ta halaka yara 4 ‘yan gida daya a Jigawa

Dutse: Gobarar wuta ta halaka yara 4 ‘yan gida daya a Jigawa

- Gobarar wuta ta yi sanadiyar mutuwar yara 4 ‘yan gida daya a Jigawa

- Kakakin hukumar tsaro ta sibil difens ya bayyana cewa ƙyallen wuta daga na'urar lantarki ya haifar da gobarar

- Kakakin ya ce lamarin ya faru ne a garin Hadeja a ranar 20 ga Janairu a misalin karfe 10:45 na dare

Wani mumunar gobarar wuta ta kashe wasu tagwaye uku tare da ɗan'uwansu a garin Hadejia da ke jihar Jigawa.

Mai magana da yawun hukumar tsaro ta sibil difens reshen jihar Jigawa, Mista Adamu Shehu, a ranar Litinin, 22 ga watan Janairu ya bayyana hakan.

Shehu ya bayyana cewa ƙyallen wuta daga na'urar lantarki ya haifar da wannan mumunar gobarar wutar.

Dutse: Gobarar wuta ta halaka yara 4 ‘yan gida daya a Jigawa
Gobarar wuta

Ya ba da sunayen tagwayen uku a matsayin, “Hassan Sale, Hussain Sale da Muhusin Sale masu shekaru biyar da haihuwa da kuma ɗan'uwansu, Aliyu Sale mai shekaru 2, dukkanin su iyali daya”.

KU KARANTA: Wuta ta cinye shaguna 50 da kwantenan kifi 30 a Kano

Ya ce wannan lamarin ya faru ne a gidan Alhaji Sale Tela na Tudun Tanda a garin Hadeja a ranar 20 ga Janairu a misalin karfe 10:45 na dare.

Kakakin ya shawarci jama'a su yi taka tsantsan yayin da suke amfani da kayan lantarki, musamman a lokacin hunturu saboda kaucewa gobarar wuta.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa Wannan: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel