Karya ta kare: An cafke wasu 'yan kungiyar asiri suna tsaka da gudanar da taro da talatainin dare

Karya ta kare: An cafke wasu 'yan kungiyar asiri suna tsaka da gudanar da taro da talatainin dare

- An cafke 'yan kungiyar asiri yayin da suke tsaka da gudanar da taro da talatainin dare

- An cafke 'yan kungiyar asirin ne a jihar Legas

- Jami'an hukumar tsaro mai yaki da aiyukan ta'addanci a jihar Legas (LNSC) ce ta yi nasarar cafke 'yan kungiyar asirin

Jami'an hukumar tsaro mai yaki da aiyukan ta'addanci a jihar Legas (LNSC) ta yi nasarar cafke wasu 'yan kungiyar asiri yayin da suke tsaka da gudanar da taro da talatainin dare a unguwar Eputu dake karkashin karamar hukumar Ijebu-Lekki dake jihar Legas.

Karya ta kare: An cafke wasu 'yan kungiyar asiri suna tsaka da gudanar da taro da talatainin dare
'Yan kungiyar asiri da aka kama

Shugaban hukumar LNSC, Mista Lateef S. O., ya ce ya bayyana cewar 'yan kungiyar asirin sun dade suna aikata miyagun laifuka a yankin na Ijebu-Lekki, tare da bayar da tabbacin cewar, nan bada dadewa ba ragowar abokan 'yan kungiyar za su shigo hannun hukumar.

DUBA WANNAN: Matasa miliyan daya zasu samu rancen kudi daga bilyan N10 da gwamati ta ware karkashin sabon shirin NEPRO

Kazalika, shugaban karamar hukumar, Ijebu-Lekki, Honarabul Dakta Kemi Surakat, ya gane ma idanunsa 'yan ta'adan kafin a wuce shelkwatar hukumar LNSC ta jihar Legas.

Dakta Surakat ya ce gwamnatin jihar Legas ba za ta bar 'yan ta'adda su ci karensu babu babbaka ba a jihar. Sannan ya kara jaddada aniyar gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyin jama'ar karamar hukumar Ijebu-Lekki.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng