Yanzu-yanzu: An damke malami da sassan jikin mutum

Yanzu-yanzu: An damke malami da sassan jikin mutum

Jami'an yan sanda a yau Talata sun damke wani malami mai suna, Alfa Kayode Abdul-Fatai, a unguwar Alakuko jihar Legas da sassan jikin mutum har da farjin mace.

Malamin wanda aka kama a gidam mai lamba No. 4, Okedumola Street, Off Obadare da zuciya da cinyan mace.

Kakakin hukumar yan sanda jihar Legas, SP Chike Oti, ya ce an damke malamin ne bisa ga labarin da aka samu ta hanyar bincike.

Yanzu-yanzu: An damke malami da sassan jikin mutum
Yanzu-yanzu: An damke malami da sassan jikin mutum

Oti ya ce yayinda aka yi masa tambayoyi ya bayyana cewa wani abokinsa ne ya bashi sassan jikin kuma shi ma an kama shi.

KU KARANTA: Anyi girgizar kasar a birnin Madina

Kwamishanan yan sandan jihar, Edgal Imohimi, ya yi kira ga mutane sun san abinda makwabtansu ke yi kuma su kawo kara ga jami'an tsaro.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel