Legas: NASFAT ta tallafawa al'ummar Hausawa a fannin kiwon lafiya

Legas: NASFAT ta tallafawa al'ummar Hausawa a fannin kiwon lafiya

- Kungiyar NASFAT reshen jihar Legas ta tallafawa al'ummar Hausawa mazauna Legas a fannin kiwon lafiya

- Kungiyar ta gudanar da wannan shirin ne tare da haɗin gwiwar kungiyar likitocin Islama ta Najeriya (IMAN)

- Fiye da mutane 400 da yara kanana 270 ne suka amfana da shirin

Kungiyar Nasrul-Lahi-L-Fatih na Najeriya (NASFAT) sashen zakat da sadaqat (NAZAS) za ta gudanar da gwaji a kan kiwon lafiya da kuma ba da magunguna kyauta ga al'ummar Hausawa da ke zaune a yankin Amuwo-Odofin na jihar Legas.

Legit.ng ta tattaro cewa, wannan shirin kiwon lafia ita ce na biyu da aka gudanar a cikin shirin NAZAS kuma an gudanar da ita ne tare da haɗin gwiwar kungiyar likitocin Islama ta Najeriya (IMAN) a Amuwo Odofin, Legas.

Fiye da mutane 400 da yara kanana 270 ne suka amfana da shirin.

Legas: NASFAT ta tallafawa al'ummar Hausawa a fanin kiwon lafiya
Taron kungiyar Nasrul-Lahi-L-Fatih na Najeriya (NASFAT)

KU KARANTA: Gwamnati ta ki cewa komai kan rashin lafiyar Yaron Shugaban kasa

Shugaban IMAN, Dokta Mustapha Alibi wanda kuma shine babban darakta a asibitin ‘National Orthopedic Hospital’, Igbobi ya jagoranci tawagar likitocin tare da wasu kwararrun likitoci 20. NAZAS, wanda aka kafa a shekara ta 2014, ta rarraba fiye da N131.5 miliyan kyauta a matsayin tallafi ga kimani mutane 516.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa Wannan: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel