Shugabannin da suka kafa PDP a APC za su dawo ba da daɗewa ba - Inji Bode George

Shugabannin da suka kafa PDP a APC za su dawo ba da daɗewa ba - Inji Bode George

- Tsohon mataimakin shugaban PDP ya ce da sauran manyan jam’iyyar APC da zasu dawo PDP

- George ya gargadi jagorancin jam'iyyar PDP akan musayar ‘yan takarar jam’iyyar

- George ya ce akwai sauran jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar APC da yawa da zasu dawo

Bode George, jigo na jam'iyyar PDP, kuma dan takarar shugabancin jam’iyyar, ya yi ikirarin cewa wasu shugabanni da suka kafa PDP wadanda a halin yanzu suna jam'iyyar APC, za su dawo kamar yadda tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya yi.

Tsohon mataimakin shugaban jam’yyar na PDP ya ce hakan yayin da yake jawabi ga manema labarai a Katsina a ranar Lahadi, 27 ga watan Nuwamba.

Legit.ng ta tattaro cewa, George kuma ya gargadi jagorancin jam'iyyar ta yadda ba za a musayar kowa ba domin jam'iyyar ta kasance ga dukkan 'yan Najeriya.

Wasu shugabannin da suka kafa PDP a APC za su dawo ba da daɗewa ba - Inji Bode George
Bode George, jigo na jam'iyyar PDP

Ya ce: "Yayin da gidanka yake yoyo, shin za ka yi watsi da ita ne ka koma zama dan haya?”

KU KARANTA: 2019: Sharuddan da Atiku zai cika kafin mu ba shi Takara – Walid Jibrin

"Za ka gyara kuma ka zauna a gidan saboda kai maigidan ne. Domin idan ka kasance mai haya a ko'ina, mai gida zai iya fitar da kai a kowane lokaci”.

'' Saboda haka, yana ƙoƙari ya dawo gida, gidan da suka gina, gidan da suka kasance sune tushen ta. Akwai sauran jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar da yawa da zasu dawo. Bari su zo”, inji shi.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa Wannan: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng