Rikita-Rikita: Kasar Koriya ta arewa ta sake harba makaman Nukiliya 3

Rikita-Rikita: Kasar Koriya ta arewa ta sake harba makaman Nukiliya 3

Alamu dai na nuna cewa rikicin yan kin kasar Koriya bai ma kama hanyar karewa ba bayan da kasar nan ta Koriya ta Arewa ta sake harba manyan makaman Nukiliya har guda uku a jiya Juma'a duk kuwa da shiga tsakani da majalisar din kin duniya ta ke yi.

Kasar ta Koriya ta Kudu dai ita ce ta bayyana cewa makaman da makwafciyar ta ta harba ta harbo su ne daga yankin kasar na Gangwon kuma sai da suka ci zangon kilo mita 250 ko ka fin daga bisani su fada cikin ruwa.

Rikita-Rikita: Kasar Koriya ta arewa ta sake harba makaman Nukiliya 3
Rikita-Rikita: Kasar Koriya ta arewa ta sake harba makaman Nukiliya 3

Legit.ng ta samu dai cewa ana ci gaba da takun saka ne a tsakanin kasashen Amurka da ke da sansanin soji a kasar Koriya ta Kudu da kuma Koriya ta Arewa ne tun bayan da kasashen biyu suka fara wata matsananciyar gaba bayan gama yakin duniya na biyu.

Tuni dai majalisar dinkin duniya ta kakabawa kasar ta Koriya ta Arewa takunkumi amma hakan bai sa shugaban ta hatsabibi mai taurin kai ya janye kai hare-haren sa da kuma gwaje-gwajen makaman kasar sa masu linzami ba.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng