An cafke wasu Yahoo boy ciki har da ‘yan Najeriya a Ghana (Hotuna)

An cafke wasu Yahoo boy ciki har da ‘yan Najeriya a Ghana (Hotuna)

- Hukumar ‘yan sandan kasar Ghana ta sanar cewa ta kama wasu ‘yan damfarar mutane a yanar gizo cikinsu har da ‘yan Najeriya

- Kimani mutane 26 ake zargi da aikata laifin damfarar

- ‘Yan sanda sun kwace kwamfyutoci da wayoyin salula da kuma wasu kayan aiki daga mutanen

Hukumar ‘yan sanda ta kasar Ghana tace ta kama wasu ‘yan damfarar mutane a yanar gizo wadanda aka fi sani da ‘Yahoo boys’ ciki har da 'yan Najeriya a ranar juma’a, 25 ga watan Agusta.

A cewar wasu rahotanni a shafuka ta yanar gizo na kasar Ghana, kimanin mutane 26 ciki har wasu ‘yan Najeriya daga cikinsu ake zargi da aikata laifuka na damfarar mutane a yanar gizo.

Wadanda ake tuhuma, wadanda shekarunsu suka kasance daga 19 zuwa 35 aka kama daga wani yanki na Ashale Botwe kusa da Madina a garin La-Nkwantanag / Madina na Greater Accra.

An cafke wasu yahoo boy ciki har da ‘yan Najeriya a Ghana (Hotuna)
'Yahoo boys masu damfarar mutane a yanar gizo

KU KARANTA: Uwa da 'yar ta da suka cillar da jariri sun sami tikitin zaman kurkuku a Katsina

'Yan sanda sun kwace kwamfyutoci 33, wayoyin salula 26 da kuma adadin sakonni daga masu tuhuma.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng