Miji na ya dage sai mun cigaba da zaman zina bayan ya sake ni saki 3 - Mata ta shaidawa kotu

Miji na ya dage sai mun cigaba da zaman zina bayan ya sake ni saki 3 - Mata ta shaidawa kotu

Wata mata mai suna Fatima Larai Ndako ta shigar da kara a wata kotu dake zama a Gwagwalada inda ta shaidawa kotun cewa mijin ta mai suna Mustapha I Sulaiman ya dage sai sun ci gaba da zama bayan yayi mata saki uku ringis.

Ita dai Ndako ta shigar da karar ne a kotun inda kuma ta roki alkalin da ya raba auren su mai shekara biyar tun da dai minjin nata ya sake ta har sau uku kuma zaman na su ya haramta.

Miji na ya dage sai mun cigaba da zaman zina bayan ya sake ni saki 3 - Mata ta shaidawa kotu
Miji na ya dage sai mun cigaba da zaman zina bayan ya sake ni saki 3 - Mata ta shaidawa kotu

Legit.ng ta samu cewa alkalin kotun mai suna Musa Umar Angulu ya ce duk da yake cewa musulunci ya bayar da dama ga miji ya saki matar sa idan hakan ya zama dole, to fa dole ne ya ci gaba da bata hakkin ta har sai ta gama idda.

Daga nan ne dai sai kotun ta yanke hukuncin lalata auren bayan da aka bukaci su sasanta kan su a wajen kotun har sau uku. Shima dai mijin yace yaji dadin hukuncin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng