Hatsari a teku: Kwalekwale ya kifa da mutane a Legas, mutum 12 sun cika

Hatsari a teku: Kwalekwale ya kifa da mutane a Legas, mutum 12 sun cika

- Kwale kwale a Legas ya kifa da wasu mutane a tafkin Legas

- An bayyana diban fasinjoji fiye da kima ne ya janyo wannan hatsari

Wani hatsarin teku ya rutsa da wasu matafiya a cikin kwalekwale yayin da kwale kwalen ya kifa dasu, wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwar mutane 12, inji rahoton Premium Times.

Shugaban hukumar kula da ruwan Legas, Abisola Kamson ta tabbatar da faruwar hatsarin, inda ta danganta shi da diban fasinja fiye da kima, tare da cewa tashar daga inda kwalekwalen ta tashi haramtacciya ce.

KU KARANTA: Dawowar Buhari: Ana tsammanin zai fatattaki ‘Kurayen’ dake zagaye da shi

Shugaban hukumar ta shaida ma majiyar Legit.ng cewa an ceto mutum hudu daga cikin wadanda hatsarin ya rutsa dasu, kuma tuni suna samun kulawa a asibiti, yayin da ana cigaba da neman sauran a cikin ruwa.

Hatsari a teku: Kwalekwale ya kifa da mutane a Legas, mutum 12 sun cika
Kwalekwale a Legas

Sai dai shugaban hukumar ta janyo hankalin hukuma kula da hanyoyin ruwa ta kasa, NIWA, data mutunta hukuncin kotu data baiwa jihar Legas daman kulawa da hanyoyin cikin ruwanta, wanda tace hakan en zai baiwa gwamnatin daman gudanar da ayyukanta yadda ya dace.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng