Da sallah ta matso sai mijina ya gudu - Wata mata ta kai kara kotu

Da sallah ta matso sai mijina ya gudu - Wata mata ta kai kara kotu

Wata mata mai suna Risikat Ojo ta kai karar mijinta Mathew Ojo a wata karamar kotu inda ta shaidawa kotun cewa mijin nata yana guduwa da ga gida a duk lokacin da bukukuwan salla suka karato don kawai kar ya kashe masu kudi.

A ranar Talatar da ta gabata ne dai matar ta maka mijin nata a kotun dake zama a garin Agodi na jihar Ibadan inda ta bukaci kotun da ta tilastawa mijin nata ya sake ta tun da wuri kafin lokaci ya kure.

Da sallah ta matso sai mijina ya gudu - Wata mata ta kai kara kotu
Da sallah ta matso sai mijina ya gudu - Wata mata ta kai kara kotu

Legit.ng ta samu cewa Risikat Ojo ta shaidawa alkalin kotun cewa: "Tun farko ma dai har yanzu mijin nawa bai biya ni sadaki na ba kuma da zarar salla ta matso to fa ban kasa sa shi a ido na har sai ta wuce da kamar kwana 7 sai kawai ya dawo."

Daga karshe dai alkalin kotun Cif Mukaila Balogon bayan ya gama sauraron duka bangarorin ya yanke shawarar raba auren nasu bayan ya gano cewa tabbas soyayya ta kare a tsakanin su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng