Game da daukar ma'aikata! Ma'aikatar NNPC tayi karin haske tare da gargadi

Game da daukar ma'aikata! Ma'aikatar NNPC tayi karin haske tare da gargadi

Ma'aikatar nan ta gwamnatin tarayya dake da alhakin kula da albarkatun man fetur ta kasa watau Nigerian National Petroleum Corporation (NNPC) a turance ta fitar da sanarwa tana mai kara jaddada wa mutane cewa ita fa bata fitar da wata sanarwar daukar aiki ba a halin yanzu.

Wannan kiran na hukumar ta Nigerian National Petroleum Corporation (NNPC) na zuwa ne a dai dai lokacin da ake ta kara samun wasu bayanan karya da aka ce daga hukumar ne suke dada kara yawo a kafafen sada zumunta.

Game da daukar ma'aikata! Ma'aikatar NNPC tayi karin haske tare da gargadi
Game da daukar ma'aikata! Ma'aikatar NNPC tayi karin haske tare da gargadi

Legit.ng ta tsinkayi jami'in hukumar dake magana da yawunta Mista Ndu Ughamadu yana bayyana cewa takardar da take yawon da kuma take dauke da sa hannun jami'an hukumar ta karya ce don haka mutane su kula kada su faa a tarkon yan damfara.

Mista Ndu ya kuma ce yan Najeriya su kwantar da hankalin su don kuwa idan hukumar zata dauki aiki to zata yi shela ta kafafen sadarwar da suka dace sannan kuma za'ayi gaskiya a cikin shirin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng