Yarbawa dake zaune a arewa sun nesanta kansu daga neman jumhuriyar Oduduwa

Yarbawa dake zaune a arewa sun nesanta kansu daga neman jumhuriyar Oduduwa

- Kungiyar Yarbawa na Yoruba Liberation Command ta yi kira ga yankinsu das u nemi jumhuriyar Oduduwa, wata sabuwar kasa

- Alúmmaan Yarbawa dake zaune a jihohin arewa 19 dake kasar sun nesanta kansu daga wannan fafutukar

- Sun kuma karyata cewan a nemi shawarar su kafin a sanar da fafutukar jumhuriyyar Oduduwa

Alúmman Yarbawa dake zaune a yankin arewacin Najeriya sun gargadi wadanda ke fafutukar neman jumhuriyar Oduduwa cewa su babu hannunsu a ciki.

Karkashin jagorancin Dr Jimoh Aiyelangbe, mukadashin shugaban kungiyar, Yarbawa dake zaune a jihohi 19 na arewacin kasar harda Abuja, sun nesanta kansu daga fafutukar.

Da yake Magana a Kano don maida martini ga kira da kungiyar Yoruba Liberation Command (YOLICOM), Aiyelangbe yace baá taba tuntubar sa a kan abu makamancin wannan ba.

Yarbawa dake zaune a arewa sun nesanta kansu daga neman jumhuriyar Oduduwa
Yarbawa dake zaune a arewa sun nesanta kansu daga neman jumhuriyar Oduduwa

A baya Legit.ng ta rahoto cewa bayan masu fafutukar neman Biyafara, wata kungiya daga kudu maso yamma, Yoruba Liberation Command (YOLICOM) ta kaddamar da son rabewa daga Najeriya.

KU KARANTA KUMA: Aisha Buhari za ta ziyarci jihar Imo a gobe LarabaAisha Buhari za ta ziyarci jihar Imo a gobe Laraba

Kungiyar wacce tayi kaddamarwan a jihar Lagas a ranar Alhamis, 27 ga watan Yuli, tace zata kafa kasar Oduduwa.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng