Dandalin Kannywood: Sana'a 1 da tafi yin fim kawo kudi - Inji Adam Zango

Dandalin Kannywood: Sana'a 1 da tafi yin fim kawo kudi - Inji Adam Zango

Shahararren jarumin nan na wasan finafinan Hausa kuma mawaki dake a arewacin Najeriya Adam A. Zango ya bayyana cewa a duk Najeriya sana'a daya ce kawai tafi harkar fim kawo kudin kashewa.

Shahararren jarumin ya bayyana cewa harkar man fetur ce kawai ke kawo kudin da suka zarce na harkar fin a kasar nan a cikin wata zantawar da yayi da gidan rediyon nan na BBC.

Dandalin Kannywood: Sana'a 1 da tafi yin fim kawo kudi - Inji Adam Zango
Dandalin Kannywood: Sana'a 1 da tafi yin fim kawo kudi - Inji Adam Zango

Legit.ng ta samu labarin cewa jarumin kuma har ila yau ya bayyana cewa fim din nan nasa na Gwaska ya kawo masa makudan kudade fiye da duk yadda ya taba samu a fina finan sa na baya.

Haka ma jarumin ya bayyana wakar nan ta 'Gumbar Dutse' da ta shahara a bakunan mutane a arewacin kasar a matsayin wadda yafi so a cikin dukkan wakokin sa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng