Dandalin Kannywood: Rashin lafiya mai tsanani ta kama jaruma Jamila Nagudu

Dandalin Kannywood: Rashin lafiya mai tsanani ta kama jaruma Jamila Nagudu

Yanzu haka labarin da ke zuwa mana na nuni da cewa fitacciyar jarumar nan ta masana'antar Kannywood Jamila Nagudu na kwance a asibiti.

Jarumar wadda cikakken sunan ta shine Jamila Umar an ce tana kwance a wata asibitin kudi ne dake a birnin Kaduna dake a arewacin kasar nan inda take jinyar ciwon da ke damun ta.

Dandalin Kannywood: Rashin lafiya mai tsanani ta kama jaruma Jamila Nagudu
Dandalin Kannywood: Rashin lafiya mai tsanani ta kama jaruma Jamila Nagudu

Legit.ng ta samu labarin cewa fitacciyar jarumar dai ce ta saka hoton nata a bisa kafar sada zumuntar nan na Instagram tana a kwance a gadon asibiti.

Ya zuwa yanzu kuma rahotannin da muka tattaro sun nuna mana cewa jarumar tana fama ne da citar nan ta tsakuwar ciki watau Appendix a turance kuma har ma an yi mata aiki a asibin.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng