Gombe: Gwamna Dankwambo ya nada sabon Amirul Hajj na jihar Gombe

Gombe: Gwamna Dankwambo ya nada sabon Amirul Hajj na jihar Gombe

- Gwamnatin jihar Gombe ta nada tawagar Amirul Hajj na 2017

- Tsohon Jakadan Najeriya a kasar Kuwait, Haruna Garba zai shugabanci tawagar

- Tawagar Amirul Hajj ta kunshi mutane 16

Gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Hassan Dankwambo ya nada mutane 16 a matsayin tawagar Amirul Hajj na shekara ta 2017 a jihar.

Tawagar za ta kasance a karkashin shugabancin Haruna Garba, wani tsohon Jakadan Najeriya a kasar Kuwait.

Kamar yadda Legit.ng ke da labari, tawagar Amirul Hajj sun hada da; Hon. Aishatu MB Ahmed, Hon. Usman Muhammad Ribadu, Hon. Abdullahi Pindiga, Hon. Miji Tilde, Hon. Justice Abubakar Jauro, Hon. Justice Adamu Usman, Sheik Adamu Dokoro, Sheikh Hamza Adamu Abdulhamid.

Gombe: Gwamna Dankwambo ya nada sabon Amirul Hajj na jihar Gombe
Masallacin Ka'aba

Sauran su ne; Malam Salisu Muhammad Gombe, Malam Bashir Ladan, Dr. Muhammad Lawan, Alh. Gambo Isari, Alh. Idi Maipachi, Abdullahi DanGombe Filiya da Sheik Zakariyya Ajiya wanda shine aka nada a matsayin sakataren tawagar.

KU KARANTA: Gwamnatin tarayya tayi ma jihohin Najeriya ruwa biliyoyin nairori (KARANTA)

A cikin wata sanarwa dauke da sanya hannun mukaddashin sakataren gwamnatin jihar, James Pisaghi JP, gwamna Dankwambo ya bukaci tawagar da nauyin da suka hada da; sa ido ga ayyukanin hajjin bana na 2017 da kuma warware duk wani matsala da zai iya kunno kai a lokacin aikin hajji da kuma taimakawa kokarin hukumar kula da Alhazai na kasa.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng