Sanata Rabi'u Kwankwaso ya kai ziyara Mambila

Sanata Rabi'u Kwankwaso ya kai ziyara Mambila

- Sanata Kwankwaso ya kai ziyara jihar Taraba domin gani da ido

- A baya ma, Sanata kwankwaso ya kai irin wannan ziyara kudu

- An yi wa fulani kisan gilla ne a Mambila

Sanata Rabi'u Kwankwaso ya kai ziyara jihar Taraba don gani da ido kan yadda hare haren kabilanci ya tagayyara jama'ar tsaunin Mambila a jihar Taraba.

Tawagar ta Sanatan, ta jajantawa mutanen yanki, sannan ta gana da sarkin Hausawa na yankin Sardauna Dr. Shehu Audu, inda yayi kira da a zauna lafiya.

Sanata Rabi'u Kwankwaso ya kai ziyara Mambila
Sanata Rabi'u Kwankwaso ya kai ziyara Mambila. Hoto an samo shi ne sashen Hausa na VOA da ke Amurka

A baya ma dai, irin wadannan kashe kashe a jihar Osun ta saka tsohon gwamnan tattaki har zuwa inda abun ya auku, inda yayi kiran a zauna da juna lafiya.

KARANTA KUMA: Mutane sama da 1000 ne suka tagayyara a Mambila

A jihar Taraba dai, anyi munanan hare-hare kan kauyuka da suka hada da na Hausawa da na Fulani, daga wasu yan ta'adda da ake kira Mambila Milisha.

An dai kafa dokar hana fita a yankin na Sardauna da ke jihar, kuma hukumomi sun shawo kan lamarin, amma duk da haka, dubban jama'a sun rasa muhallansu.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng