Sadarwa: Kamfanin sadarwa na Etisalat ta shiga uku a Najeriya

Sadarwa: Kamfanin sadarwa na Etisalat ta shiga uku a Najeriya

- Kamfanin sadarwa na Etisalat zata fice daga Najeriya nan da makonin 3

- Shugaban kamfanin na Najeriya yace kokarin da suka yi na shawo kan lamarin abun yaci tura

- Ana bin kamfanin Etisalat na Najeriya bashin dala Amurka biliyan 1.2

Kamfanin sadarwa na Etisalat na kasa da kasa zai rufe kasuwancinsa a Nigeria ta fice daga kamfanonin sadarwar kasar nan da makonni uku masu zuwa.

Babban shugaban kamfanin wato Cif Executive Officer (CEO), Hatem Dowidar ya sanar da hakan a ranar Litinin, 10 ga watan Yuli.

Dowidar ya ce duk masu hannun jari a kamfanin Etisalat na Nigeria daga Hadaddiyar Daular Larabawa sun bar kamfanin, ciki har da mallakar asusun gwamnati Mubadala.

Sadarwa: Kamfanin sadarwa na Etisalat ta shiga uku a Najeriya
Kamfanin sadarwa na Etisalat a Najeriya

Ya ci gaba da cewa sun mika sanarwar hakan ne a rubuce ga mahukuntan kasar da sauran masu hannun jari a kamfanin.

KU KARANTA: Shugaban kasa Buhari zai dawo nan ba da jimawa ba – Olumba Olumba

Kamfanin Etisalat Najeriya ta ciwo bashin dala Amurka biliyan 1.2 daga bankunan kasar 13 wanda tun a shekarar 2013 wanda suka kasa biya har yanzu bayan shekaru hudu.

Mista Dowidar yace duk kokarin da akayi na shawo kan lamarin abun yaci tura saboda haka suka yanke shawarar ficewa daga Nigeriar

Abin tambaya a nan shine ko kamfanin Etisalat zata yi la'akarin sake zuba hannu jari a Najeriya nan gaba, Dowidar ya ce babu wata halamar haka.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng