Rikita-Rikita! Kowa yayi ta kansa, zaki 4 sun tsere daga gandun daji

Rikita-Rikita! Kowa yayi ta kansa, zaki 4 sun tsere daga gandun daji

- Kowa yayi ta kansa, zaki 4 sun tsere daga gandun daji

- Zakuna 4 sun tsere ne a kasar Afrika ta kudu

- Sun dai tsere ne tun ranar Lahadi

Mahukunta a kan kasar Afrika ta kudu na can sun dukufa ka'in da na'in wajen kokarin gano wasu zakuna hudu da suka tsre daga gandun dajin kasar.

Mahukuntan sunce zakunan kosassu ne kuma sun gudu ne tun ranar Lahadin da ta gabata sannan kumar har inda yau take ba'a gansu ba kuma ba'aji labarin su.

Rikita-Rikita! Kowa yayi ta kansa, zaki 4 sun tsere daga gandun daji
Rikita-Rikita! Kowa yayi ta kansa, zaki 4 sun tsere daga gandun daji

Legit.ng ta samu labarin cewa daga nan ne fa sai mahukuntan na kasar suka shawarci mutanen kasar musamman ma masu makwaftaka da dajin da suyi taka tsantsan.

Hakan dai na zuwa ne bayan da a cikin watan Mayu wasu zakokin guda biyar suka tsere daga wannan gandun daji.

Amma daga bisani an sake cafke hudu, sai dai har yanzu na biyar din babu labarinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng