Matsalar shaye-shaye tsakanin matan arewa ta ta'azzara

Matsalar shaye-shaye tsakanin matan arewa ta ta'azzara

- Matsalar shaye-shayen mata a arewa ta ta'azzara

- Yanzu dai matan aure, yan mata da zawarawa sun fi yin shaye-shayen

- An bukaci mutane su sa ido wajen tarbiyyar 'yayan su

Matsalar shaye-share da kuma tu'ammali da kayan maye a tsakanin matan arewacin kasar nan na kara kamari a cikin al'umma.

Wannan dai yana daya daga cikin batutuwan da hukumar hana sha da kuma fataucin miyagun kwayoyi watau NDLEA ta ke yaki da su ka'in da na'in yanzu haka.

Matsalar shaye-shaye tsakanin matan arewa ta ta'azzara
Matsalar shaye-shaye tsakanin matan arewa ta ta'azzara

Hukumar ta bayyana cewa yanzu haka dai matan aure da yan mata tare kuma da zawarawa sune kan gaba a wajen harka da kwayoyin.

Legit.ng ta samu cewa Alhaji Hamza Umar babban kwamandan hukumar da ke yaki da shan miyagu kwayoyi na jihar Kano ya ce abin ya yi matukar yawa a jihar Kano, wanda matsalar ta fi yawa a tsakanin matan aure, da zawarawa, da kananan 'yanmata, da ko biki ake sai sun tanade su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng