Ambaliyar ruwan sama ya lalata dukiyoyi a jihar Gombe

Ambaliyar ruwan sama ya lalata dukiyoyi a jihar Gombe

- Ambaliyar ruwan sama ya halaka gidaje da dukiyoyi da dama a jihar Gombe

- Ya kuma rusa gadar tafiya Biu daga Gombe

- A ranar Laraba ne aka sha ruwan sama kamar da bakin kwarya a jihar

Ambaliyar ruwan sama ya halaka gidaje da dukiyoyi da dama a jihar Gombe sannan kuma ya rufta gadar tafiya Biu daga jihar ta Gombe.

Ruwan sama ya fara zuba kamar dab akin kwarya a safiyar ranar Laraba, 5 ga watan Yuli, sannan kuma an shafe saóí da dama ana zuba ruwan wanda hakan ya yi sanadiyar da ruwan ya shiga unguwanni takwas sannan kuma ya halaka dukiyoyi da gonakin alúmma.

Shugaban hukumar kula da ayyukan bada agajin gaggawa wato SEMA, Malam Mohammed Garba ya bayyana cewa ruwan saman ya haifar da cunkoso ga ababen hawa inda motoci ke tafiya a sahu daya sakamakon ruftawar gadar.

Ambaliyar ruwan sama ya lalata dukiyoyi a jihar Gombe
Ambaliyar ruwan sama ya lalata dukiyoyi a jihar Gombe

KU KARANTA KUMA: Matsin tattalin arziki rahama ne ga Najeriya – Oyegun

Malam Garba ya kara da cewa ba’a rasa rai a ambaliyar ba amma wani wanda ke zaune a unguwar Lili dake kusa da gadar ya bayyana tsintar gawar wani yaro dan almajiri mai shekaru 16 a karkashin gada.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng