Obasanjo: Ban yi nadaman ritaya jami’an sojoji 'yan siyasa a shekarar 1999 ba – Inji Obasanjo

Obasanjo: Ban yi nadaman ritaya jami’an sojoji 'yan siyasa a shekarar 1999 ba – Inji Obasanjo

- Obasanjo ya ce bai yi nadama a kan ritayan da yayi ma wasu jami’an sojojin Najeriya

- Tsohon shugaban ya ce yayi wannan ne domin ya kare dimokuradiyya a kasar

- Obasanjo ya bayyana cewa yin haka zai taimaka wajen hana Najeriya daga wani yakin basasa

Tsohon shugaban kasar Najeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya ce ba shida wani uzuri ga ritayan wasu jami'an sojojin Najeriya wandanda suka sunduma a harakar siyasar kasar a shekarar 1999.

Kamar yadda Legit.ng ke da labari, Obasanjo ya bayyana cewa, ya yanke wannan shawarar ne domin ya kare jaririyar dimokuradiyya a kasar.

Ya bayyana hakan ne a ranar Talata, 4 ga watan Yuli a lokacin gabatar da wani littafi mai suna: "The First Regular Combatant: Birgediya Zakari Maimalari, OFR" a Abuja. Llittafin da Haruna Yahaya ya rubuta.

Obasanjo: Ban yi nadaman ritaya jami’an sojoji 'yan siyasa a shekarar 1999 ba – Inji Obasanjo
Tsohon shugaban kasar Najeriya, Cif Olusegun Obasanjo Source: @ObasanjoOAremu

KU KARANTA: Obasanjo tare da wasu gwamnoni sunyi ta’aziyya ga Ganduje kan mutuwar Danmasanin Kano

Obasanjo ya kara da cewa yiwa jami'an sojan masu alaka da ‘yan siyasa ritaya zai taimaka wajen hana Najeriya daga wani yakin basasa.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng