Alhamdulillah: Musulunci ya samu ƙaruwa

Alhamdulillah: Musulunci ya samu ƙaruwa

- Wani matashin kirista ne ya musulunta a jihar Sakkwato

- Matashin ya musulunta ne bayan ya halarci taron wa’azin Tafsiri a wani Masallaci

Gaskiya ne, duk wanda Allah yayi ma shiriya, toh ba zai taba bacewa ba, wannan shine kwatankwacin abin daya wakana a ranar Alhamis 1 ga watan Yunin 2017, kamar yadda Rariya ta samu rahoto.

Majiyar Legit.ng ta ruwaito wani matashin kirista ne ya musulunta a jihar Sakkwato bayan ya halarci taron wa’azin Tafsiri a wani Masallaci dake Unguwar Koko cikin birnin Sakkwato.

KU KARANTA: Gwamnati ta samar da dokoki guda 9 da zasu taƙaita zuƙan sigari (KARANTA)

Limamin wannan Masallaci na Ali Bn Abi Talib, Malam Bashar Ahmad Sani ne ya baiwa wannan matashi kalmar shahada, inda nan take ya musulunta kuma ya sauya suna.

Alhamdulillah: Musulunci ya samu ƙaruwa
Matashin daya musulunta

Sai dai zuwa lokacin hada wannan rahoto, bamu tabbatar da tsohon sunansa ba da kuma sunan daya canza.

Dama dai ana yawan samun jama’a wadanda ba Musulmai ba suna karbar addinin Musulunci, musamman a watan Azumi yayin da ake gabatar da Tafsirin Al-Qur’ani mai girma, don ko a Azumin bara an samu sabbin Musulmai da dama maza da mata a masallatai daban daban.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Batutuwan aure, kalla

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng