Kotu ta yanke wa wasu ‘yan luwadi 2 hukuncin bulala 85

Kotu ta yanke wa wasu ‘yan luwadi 2 hukuncin bulala 85

- Wata kotu a kasar Indonesia ta yanke wa wasu Indonesia biyu hukuncin bulala 85 a bainar jama’a don yin luwadi

- Mutanen biyu sun ce ba zasu daukaka kara a kan hukuncin ba

Wani kotun musulunci a kasar Indonesia a ranar Laraba, 17 ga watan Mayu ta yanke wa wasu maza biyu ‘yan kasar Indonesia hukuncin bulala 85 don yin luwadi.

Wani kwamitin alkalai ne suka yanke wannan hukuncin bulala wanda za a yi a idon jama’a kuma karon farko da za a gabatar da irin wannan hukunci kan yin luwadi tun da aka gabatar da dokan a shekara 2014.

Wannan jumla ya na da tsanani fiye da bulala 80 da mai gabatar da arraraki ya bukaci.

Kotu ta yanke wa wasu ‘yan luwadi 2 hukuncin bulala 85
'Yan luwadi biyu a lokacin da aka yanke masu hukunci sun rufe fuskokinsu da rigunansu da kuma hannayensu

KU KARANTA KUMA: Albishirin ku masoya Buhari ga sako daga fadar shugaban kasa (Karanta)

Kamar yadda Legit.ng ke da labari, Alkalin kotun, Khairil Jamal, ya ce a cikin sanarwasa cwaa, wadanada ake tuhuma sun tabbatar da aikata luwadin da kuma amsa laifin.

Duk da haka, mutanen biyu sun wakilci kansu a kotu kuma sun ce ba zasu daukaka kara a kan hukuncin ba.

Za a yi wa mutanen bulala a lokacin da za a gudanar da wani biki a ranar 23 ga watan Mayu, a lardin birnin Banda Aceh, inda masu sintiri suka kama su.

Kungiyoyin kare hakkin dan adam sun ce, kyamar luwadi na karuwa a kasar.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga bidiyon tsohon direban Bishof David Abioye wanda ya karbi musulunci yayin da ya yi murabus daga cocin Living Faith Church

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng