JAMB ta saki sakamakon jarrabawa

JAMB ta saki sakamakon jarrabawa

- Hukumar JAMB ta fito da sakamakon jarrabawar UTME da aka gudanar a ranar Asabar

- Rajistara na hukumar da karamin ministan Ilimi sun ziyarci wasu wuraren jarrabawar a Kogo da ke Bwari

Hukumar JAMB ta fito da sakamakon jarrabawar UTME da a gudanar a ranar Asabar, 13 ga watan Mayu.

Rajistara na hukumar, Farfesa Is-Haq Oloyede ya tabbatar da wannan labari ne yayin da yake magana a lokacin ziyarar saka idanu ga wanda suke rubuta jarrabawar UTME tare da karamin ministan Ilimi, Farfesa Anthony Anwukah a Abuja.

Oloyede da Anwukah sun ziyarci wuraren jarrabawar Digital Bridge Institute, Global Learning Institute, Sascon International School da kuma JAMB CBT Center a Kogo, Bwari.

JAMB ta saki sakamakon jarrabawa
Masu jarrabawar UTME

KU KARANTA KUMA: Shugaba Buhari ya sha ruwan addu’o’i a Jihar Legas

Legit.ng ta ruwaito cewa Oloyede ya nuna gamsuwa kan yadda ake gudanar da jarrabawar yanzu, kuma ya ce kokarin 'yan takaran babu laifi.

Rajistara na hukumar ya ce: "Sakamakon jarrabawar UTME ya fito da kuma kokarin 'yan takaran babu laifi. Amma muna tabbatar da cewa wannan shi ne sakamakon yanzu maimakon tunanin za a iya samun sakamakon ta wani hanya. "

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Femi Fani Kayode ya bayyana cikakken bayani kan maganarsa da shugaba Buhari

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng