An kashe akalla mutum 32 a Zaki Biam ta Benue
- A kalla mutum 32 ne suka mutu a garin Zaki Biam da ke karamar hukumar Ukum na jihar Benue, da ke yankin arewa ta tsakiyar Najeriya
- Lamarin dai ya faru ne a ranar Litinin bayan da wasu 'yan bindiga suka kai hari wata kasuwar doya a garin Zaki Biam da ke jihar
![An kashe akalla mutum 32 a Zaki Biam ta Benue An kashe akalla mutum 32 a Zaki Biam ta Benue](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt7hn53pu3ofr.jpeg?v=1)
Sai dai kakakin rundunar 'yan sandan jihar, Moses Yamu ya ce mutum 17 ne suka mutu yayinda wasu 11 suka jikkata.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da harin, ya kuma mika sakon ta'aziyyarsa ga 'yan uwan wadanda harin ya shafa.
KU KARANTA: Darajar Naira ta kara yin sama
Mai magana da yawun shugaban Femi Adesina, ya ce: "Shugaba Buhari ya umarci jami'an tsaro su fara binciken gaggawa da nufin hukunta wadanda suka aikata laifin."
Moses Yamu ya shaida wa majiyar mu cewa: "Da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar Litinin ne wasu mutane a cikin mota da kuma wasu a kan babura suka shiga garin kuma suka bude wa wasu 'yan kasuwa wuta."
Ya kara da cewa tuni an kara tsaurara matakan tsaro a yankin kuma tuni aka kama mutum uku wadanda ake zargin suna da hannu a harin.
Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da
Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng