An damke Khaleel Tanko Al Makura akan laifin kisan kai

An damke Khaleel Tanko Al Makura akan laifin kisan kai

An damke Mr. Khaleel Umar Al-Makura, haifaffen cikin gwamnan jihar Nasarawa, Umar Al-Makura akan laifin kisan wani dalibin makarantan gwamnati mai suna Ovye Amos, a Lafia.

To fa : An damke yaron gwamnan jihar Nasarawa akan laifin kisan kai
To fa : An damke yaron gwamnan jihar Nasarawa akan laifin kisan kai

Wani abun takaici ya faru ne a ranan Litinin a hadarin mota. Sai daliban makarantan suka fara zanga-zanga a ranan Talata domin neman a hukunta wanda kashe dalibin makarantan sakandaren.

Amma jami’ an tsaro sun yi magana da daliban domin kashe wutan abinda ya faru.

KU KARANTA: Majalisar dattawa zata fara binciken Melaye da Saraki

Jaridar Vanguard ta bada rahoton cewa Kwamishanan ilimin jihar, Aliyu Tijjani, ya fadawa daliban cewa gwamnati zata dau matakin da yakamata wajen tabbatar da cewa an hukunta yaron gwamann da ya aikata wannan abu.

“An damke shi, kuma ina mai nuna bacin raina akan abinda ya faru jiya. Abin takaici ne, da takaici sosai.”

Shugaban daliban makarantan, Goodluck Agwu, yayi bayanin cewa motar Mr. Khaleel Umar Al-Makura, ta bige yaron ne yayinda yaje sayan batirin fitilarshi.

https://www.facebook.com/naijcomhausa/#

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng