Ku kalli yadda ake hako zinare a Arewa (Hotuna)

Ku kalli yadda ake hako zinare a Arewa (Hotuna)

- Ministan ma'adanai na Najeriya watau Mr kayode Fayemi ya ziyarci inda ake hako ma'adanai musamman ma Zinare a jihar Kaduna dake arewacin Najeriya.

- A lokacin ziyarar tasa, Ministan yace: "Tabbas wannan gwamnatin da shugaba Buhari yake jagoranta tana da kyawawan manufofi musamman ma ga masu hakar ma'adanai na kasar nan."

Ku kalli yadda ake hako zinare a Arewa (Hotuna)
Ku kalli yadda ake hako zinare a Arewa (Hotuna)

Har ila yau a lokacin ziyarar tasa, ministan ya kuma je inda ake hakar ma'adanan ba bisa ka'ida ba duk dai a jihar ta Kaduna a cikin karamar hukumar Birnin Gwari.

A wani labarin kuma, Shugaban sashen nazarin harkokin cigaba na jami'ar Ibrahim Badamasi Babaginda (IBB) dake a karamar hukumar Lapai ta jihar Niger Prof. Nuhu Obaje ya sanar da samun danyen mai a yankin tekun Bida.

Farfesa Nuhu ya sanar da cewa sashen manazartan da yake jagoranta sun gano tarin danyen mai mai yawan gaske a yankin na tekun Bida duk dai a cikin jihar ta Niger a wani bincike da suka yi.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng