An kafa sabuwar rundunar sojan ruwan Najeriya a Arewa
A ci gaba da yi wa ‘yan kungiyar Boko Haram kofar rago don hana su damar shagar da makamai Najeriya, hedikwatar sojojin ruwa ta kafa sabuwar runduna a tafkin Chadi don tabbbatar da tsaro.
![An kafa sabuwar rundunar sojan ruwan Najeriya a Arewa An kafa sabuwar rundunar sojan ruwan Najeriya a Arewa](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt1uflgsa2174o.jpeg?v=1)
An gano cewa ‘yan Boko Haram na shigar da makamai cikin Najeriya daga ruwan tafkin chadi, hakan yasa gwamnatin tarayya ta umarci sojojin ruwa da su bude runduna a gurin, a cewar daraktan labarai a hedikwatar sojojin ruwan Najeriya, Kaftin Sulaiman Dahun.
KU KARANTA: An gano gunkin Firauna a kasar Misra
Baya ga tafkin Chadi, rundunar sojan ruwan ta kuma kakkafa ‘karin wasu rundunonin a sauran sassan Najeriya. Haka kuma rundunar ta yi tunanin bude sabbin rundunoni a duk inda ake da babban kogi a fadin kasar.
Masanin tsaro Saleh Jingir mai ritaya, ya ce kafa runduna da sojojin ruwa su kayi a yankin tafkin Chadi wani abu ne mai matukar muhimmanci, ganin yadda ake amfani da ruwan wajen shigar da makamai.
Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da
Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng