Fari: Yunwa ta kashe mutane 110 a wannan kasa cikin sa’oi 48
Kamfanin Dillancin Labarun ya kalato shugaban kasar Somaliya inda ya sanar da mutuwar mutane 110 saboda yunwa.
![Fari: Yunwa ta kashe mutane 110 a kasar Somalia cikin sa’oi 48 Fari: Yunwa ta kashe mutane 110 a kasar Somalia cikin sa’oi 48](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt35pq5r3puu4g.jpeg?v=1)
shugaban na Somaliya Khairi da ya fitar da bayani a ranar asabar ya fadi cewa; Mutanen da su ka mutu sun rika yin gudawa mai tsanani, a yankin kudancin kasar.
Ya ci gaba da cewa; Wajibi ne ga mutane kasar ta Somaliya a duk inda su ke da su taimakawa ‘yan’uwansu ‘yan kasar mabukata da su ke fama da yunwa.
KU KARANTA: Daki daki, alƙalumman ɓarnar da Boko Haram suka yi jihar Borno
![Fari: Yunwa ta kashe mutane 110 a kasar Somalia cikin sa’oi 48 Fari: Yunwa ta kashe mutane 110 a kasar Somalia cikin sa’oi 48](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt4qvlrevjvv.jpeg?v=1)
Har ila yau, shugaba ya ci gaba da cewa; “Aikin da ke gaban hukuma shi ne taimakawa mutanen da fama da yunwar, saboda farin da kasar ta ke fama da shi.”
A yankin al-Bay na kasar mahukunta sun sanar da mutuwar mutane 69 mafi yawancinsu kananan yara da tsofaffi.
Tun a karshen watan Febrairu ne dai gwamnatin kasar ta Somaliya ta sanar da halin ko ta kwana saboda fari mai hatsari da kasar ta ke fama da shi.
Mutane miliya 3 ne dai farin ya jefa cikin yunwa kamar yadda kungiyoyin fararen hula su ka ambata.
Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng