Ana take mana hakin mu na sanya hijabi – Matan musulmai

Ana take mana hakin mu na sanya hijabi – Matan musulmai

- Wani kungiyar matan musulmai tayi ikirarin cewa anan take musu hakkin su

- Game da cewar kungiyar, ce musu su bayyana kunnuwa da kawuna kafin iya zama jarabawa ko rijista take hakkinsu ne na lullube jikinsu a matsayin matan musulmai

Ana take mana hakin mu na sanya hijabi – Matan musulmai
Ana take mana hakin mu na sanya hijabi – Matan musulmai

Wata kungiyar matan musulmai karkashin hakkin sanya hijabi tayi bayani a ranan Laraba,1 ga watan Febrairu, cewa ana take musu hakkinsu na sanya hijabi a ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu.

Kungiyar ta bayyana cewa yawancin mata masu sanya hijabi basu samun aiki da wasu dama a wannan kasa,duk da cewan sun cancanci a basu wadannan ayyuka.

Game da cewar jaridar Punch, shugabn kungiyar, Hajia Mutiat Orolu-Balogun, tace ana tilastawa matan musulmai su bayyana kunnuwansu da kawunansu kafin su zauna jarabawan JAMB ko rijistan BVN.

KU KARANTA: Soja ya hallaka wani dan achaba

Orolu-Balogun yace: “ Yi tunanin ace ka cire rigarka saboda zaka amsa lasisin tukin mota, ko ace ba zaka iya zabe ba sai kan nonuwanki ya fito a katin zabe.

“Wannan,da kuma fiye da haka ne yan matan musulmai ke fukanta idan aka ce ta cire hijabin ta kafin a bari ta zantar da hakkin dan adam din ta."

Tace sanya hijabi wajabcin addini ne ba al’adan larubawa ba da mutum zai yi lokacin da ya ga dama. Wata matar , Hajia Hafsah Badru, tayi kira ga kafofin yada labarai cewa suyi gaskiya wajen ruwaito labaan da ya shafi hijabi.

Tace: “ Gayawa ma mace ta cire hijabinta zalunci ne gareta; bai kamata a ce ana irin wannan a kasa irin Najeriya ba.”

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng