ABIN TAUSAYI: Mutane 5 suka hallaka a wata hatsarin wuta (HOTUNA)
Wani matashi mai suna Sarafa Lasisi da iyalinsa a garin Koko ta jihar Kebbi sun hallaka a wata mummunar hatsarin wuta a gidansu.
![ABIN TAUSAYI ABIN TAUSAYI](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt5org6cobs1r.jpeg?v=1)
A ranar Talata, 10 ga watan Janairu 2017 ne wannan hatsarin ya auku a inda wani daga cikin ɗan'uwan matashin ya sanar da aukuwar hadarin a shafinsa ta Facebook. An rahoto cewa shi mutumin da matarsa da 'ya'ya uku ne suka hallaka a wannan hadarin.
![ABIN TAUSAYI ABIN TAUSAYI](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt46m2esg40j8.jpeg?v=1)
Wani daga cikin dan’uwan marigayi kuma mai suna Don Baba ya wasa wasu hotunonin margayin a shafinsha a inda yake bankuana da marigayin.
Kuma wani mutum, Abdulrauff Mustapha, shi ma ya saka wasu hotunonin hadarin wutar a shafinsha.
Inda ya ke cewa: “Allah ya sa al janat Firdausi ne makomar sa da iyalansa Amin ya Allahu. Wannan babban asara ne ga duk dangin gaba daya.''
![ABIN TAUSAYI ABIN TAUSAYI](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt29smoqmmf9p.jpeg?v=1)
Lalle, wannan wata babbar asara ce!
Ku kasance tare da mu@ https://www.facebook.com/naijcomhausa
http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng