Babban abun mamaki da al'ajabi a kasar Jamus (Karanta)

Babban abun mamaki da al'ajabi a kasar Jamus (Karanta)

Kungiyar RB Leipzig ta sake komawa mataki na daya a kan teburin Bundesliga na Jamus, bayan da ta ci Hertha Berlin 2-0 a ranar Asabar.

Babban abun mamaki da al'ajabi a kasar Jamus (Karanta)
Babban abun mamaki da al'ajabi a kasar Jamus (Karanta)

Timo Werner ne ya fara ci wa kungiyar kwallon kuma na tara da ya ci kenan a gasar ta Bundesliga ta bana, sannan mai tsaron baya, Naby Keita ya ci ta biyu.

Da wannan sakamakon, RB Leipzig, wadda ta shigo gasar Bundesliga a bara, ta bai wa Bayern Munich tazarar maki uku.

A wani labarin kuma, Manchester City ta doke Arsenal 2-1 a Etihad a wasansu na mako na 17 ranar Lahadi, abin da ya sa City ta zama ta biyu a tebur da maki 36, a bayan Chelsea mai 43.

Arsenal wadda ta fara cin kwallo a minti biyar kacal da shiga fili ta hannun Walcott, yanzu ta dawo ta hudu a tebur da maki 34.

Minti biyu da dawowa daga hutun rabin lokaci ne sai Leroy Sané ya rama wa Manchester City, kafin kuma a minti na 71 Raheem Sterling ya ci ta biyu.

Sai dai kuma zaman Mancester Cityn a matsayi na biyu zai iya zama na wucin-gadi kafin ranar Litinin, inda Liverpool za ta iya kawar da ita, idan ta yi nasara a gidan Everton.

Yanzu Arsenal ta maye gurbin Manchester City na da, matsayi na hudu a tebur.

Ku biyo mu a tuwita: @naijcomhausa

Ku biyo a shafin fezbuk: Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng