Abin al’ajabi: An haifi jaririya da kawuna 2 a Legas

Abin al’ajabi: An haifi jaririya da kawuna 2 a Legas

- Wannan shine lokacin farko da zan ga irin wannan abu

- Wannan wani irin abu ne da ke faruwa wanda likitoci ke kira da Parapagus

Abin al’ajabi: An haifi jaririya da kawuna 2 a Legas
Abin al’ajabi: An haifi jaririya da kawuna 2 a Legas

Mutanen unguwan Ogudu a jihar Legas sun ga abin al’ajabi yayinda aka hafi wata jaririya da kawuna biyu.

Game da cewan rahotanni, jariryar mai kawuna biyu da iskar nishi na bature a kowani kai. Tana da wuya daya, kirji daya, kafafu da hannuwa 2. Wannan wani irin abu ne da ke faruwa likitoci sun ace masa Parapagus.

Likitocin asibitin Med-In Specialist Hospital, Osogbo Street,wadanda suka ciro jariryar sun bayyana cewa an Haifa jaririyar ne mislain karfe 6:30 na yamma a ranan Talata ta hanyar tiyata.

KU KARANTA: Ana son bata mini suna- Babachir

Jaridar The Nation ta bada rahoton cewa a asibitin ranan Laraba, an tayar da jariryar kuma an kaita asibitin Jami’ar jihar Legas domin kula.

Game da cewan wata ma’aikaciyar sibitin da suka ciro ta, sun shiirya ciro yan biyu ne amma abin mamaki sai suka ansu a hada.

“Wannan shine lokacin farko da zan ga irin wannan abu. Na kasance ina kallo a Fi mamma ban taba gani a gaske ba . Amma,an gode likitan yace sun rayu.

“A yanzu da nike muku Magana, mahaifiyarsu bata san halin da suke ciki ba. Tana jiran ne kawai ta dauki yan biyun ta. Bamu fada mat aba tukunna. Mijinta ne kawai aka fada mawa kuma yana tare da likitocin yayinda aka kaisu asibitin Jami’ar Legas.”

Ku kasance tare da mu@ https://www.facebook.com/naijcomhausa, https://www.twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng