An tsirar da mata da yara guda 8 daga hannun boko haram

An tsirar da mata da yara guda 8 daga hannun boko haram

- Wasu mafarauta a Adamawa sun tsirar da wasu mata da yara guda 8 daga hannun Boko Haram dake dajin nan mai hadari na Sambisa

- Matan da yaran an kai so gurin hukumomin tsaro dan kai rahoto

Wasu jaruman mafarauta sun tsirar da mata 5 da yara 3 daga hannun yan ta'addan boko haram da ke kame a dajin Sambisa.

Jaridar premium times ta ruwaito mana cewa, Garba Tarfa shugaban kungiyar mafarautar na jahar Adamawa yace  wadanda suke kamen an tsirar da su makon da taci gabata.

An tsirar da mata da yara guda 8 daga hannun boko haram

Mutanen mu sun tsirar da matan da yaran makon da ya gabata dai dai sun fito da gudu, yayin  dauki sojojin mu suke dauki ba dadin barin wuta da yan boko haram.

Tarfa yace" a halin yanzu dai mun kai matan da yaran gurin hukumar da ta dace dan basu kulawa ta musamman, sun bada labarai mara dadi a kan dajin Sambisa.

KU KARANTA:  Babban dan wasan duniya zai shiga kurkuku.

Tsiratar da wadan nan mutanen 8  yazo mako 1 da tsirar da wasu mutane 14 wanda mafarautar yan banga suka yi a yayin barin wuta tsakanin  sojoji da yan kungiyar ta boko haram.

Mai magana da yawun bakin yan sanda na shiyar Adamawa ya tabbatar da ceto su da akayi, lalle munji cewa mafarautan sun tsirar da su, amma har yanzu ban samu cikakken bayani ba.

In zaka iya tunawa Boko Haram sun saki yan matan chibok 21 bayan yarje-jeniyar da suka yi da gwamnati.

Duk da yake har yanzu ba muji taka mai man abunda aka tattauna a yarje-jeniyar kafin sakin yan matan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng