Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako
Jaridar Legit.ng ta tattaro muku muhimman labarai da suka faru a Najeriya a karshen makon da ya gabata
1. Uwa,’ya, da jika sun hallaka a hadarin kwale-kwale
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt39u5po7480pg.jpeg?v=1)
Akalla mutane 7 ne suka rasa rayukan su a wata hadarin jirgin kwale-kwale da faru a rafin Gbako a Karamar hukumar Katcha a jihar Neja.
2.‘Yan Najeriya na bakin cikin kisan Kanan Abu Ali da Boko Haram tayi
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt679mbq3cb0o.jpeg?v=1)
Labarin da aka samu a safiyar jiya, 5 ga watan Nuwamba akan kisan Laftanan Kanal Muhammad Abu ali , ya tayar da bakin cikin a fadin kasa ga baki daya.
3. Matsin tattalin arziki ya hana shigowa da motoci Najeriya
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt3r35ualbd87g.jpeg?v=1)
Matsin tattalin arziki da wahalan canjin kudi ya shafi sana’ar shigo da motocin Najeriya ta tashar jirgin ruwa. Game da cewar Manajan ayyuka na ma’aikatar tashan jirgin ruwa, Mr Jack Angrish ne ya ce shigo da kaya ya ragu daga 30,000 zuwa 6,000 a watanni 6 da suka gabata.
4. Dukkan ku zabi ne – MASSOB ga shugabannin Igbo
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt3sr7f9hf6jj.jpeg?v=1)
Kungiyar fafutukar neman Biafra wato Movement for the Actualization of Sovereign State of Biafra (MASSOB) ta siffanta wadanda basu goyon bayan manufar Igbo na samun yanci a matsayin zabi.
5. Yan bindiga sunyi garkuwa da mutane 5 a jihar Ekiti
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt5o5tcfipu9c.jpeg?v=1)
Anyi garkuwa da mutane 5 a jihar Ekiti, jihar mai maganan nan Ayo Fayose a ranan asabar, 5 ga watan Nuwamba 2016. Game da cewar NAN, wadanda akayi garkuwa da su sune Fasto Ojo da direbansa da kuma wasu guda 3.
6.Sanata Omisore yayi aman N350m ga EFCC
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt6gtuvo71cf3.jpeg?v=1)
Tsohon mataimakin gwamnan jihar Osun ya dawoda kudi N350m daga cikin N1.7 billion na rashawan zaben jihar Ekiti da kuma badakalar kudin makamai zuwa ga hukumar hana almundahana da yima tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta yi masa
7.EFCC ta haramta kawowa Fani-Kayode ziyara
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkytj10ajf449gg.jpeg?v=1)
Hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC ta haramta kawo ma firsinoni ziyara. Jaridar vanguard ta bada rahoton cewa an hana dukkan firsinonin EFCC kiran iyalan su da amsoyan su.
8.Babban titin Lagos- Ibadan ya samu lafiyar tafiya - FRSC
![Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako Abubuwan da suka faru a Najeriya a karshen mako](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt6c9oi9nmdir.jpeg?v=1)
FRSC tana tabbatar ma masu bin titin Lagos - Ibadan cewa motoci zasu iya zurga-zurga duk da gyaran da ake a sashen da yafi cinkoso.
Asali: Legit.ng