Fastonmu yayi lalata da ni - Yvonne Smith

Fastonmu yayi lalata da ni - Yvonne Smith

Wata budurwa ta tona asirin wani fasto wanda ya tilasta ta yayi lalata da ita da sunan karama.

Fastonmu yayi lalata da ni - Yvonne Smith

Matar yar kasan South Afrika mai suna Yvonne Smith, ta tuhumci fasto Bongani Manyisa da yin lalata da ita bayan yayi mata addu’a.

Matar ta je wajen faston ne saboda tana neman taimako akan ciwon bugun jini amma sai da ta biya shi kudi N453,000 da kuma kwanciya da ita. Game da cewar ta, yace za’ayi watanni ana addu’an amma ya kasance yana lalata da ita da sunan nema mata lafiya.

KU KARANTA: Kuyi hattara da Sojoji: Kungiyar fafutuka ga Tsageru

Smith tace ta yanke shawaran tona masa asiri ne daga baya. Kuma ta fadawa shugabannin cocin kuma an kore shi.

Ga abinda tace: “Na kasance inada ciwon gudun jinni tun agustan da ya gabata. Ina zuwa asibiti amma babu wani canji. Sai aka gayyace ni coci inda faston ya mini addu’a. bayan na samu sauki, sai faston ya fara lalata da ni har nace na gaji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng