Dalilin daya sa muka ce Jimoh Ibrahim - INEC

Dalilin daya sa muka ce Jimoh Ibrahim - INEC

- INEC tace dalilin daya sa tace Jimoh Ibrahim shine dan takarar PDP a zaben gwamnan jihar Ondo da za'a yi ranar 26 ga Nuwamba bin umurnin babbar kotun kasa ne

- Hukumar zaben tace idan kotun dake gaba da wannan ta bada umurnin aba Jegede, zata bi umurnin kotun

Dalilin daya sa muka ce Jimoh Ibrahim - INEC

Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta tayi bayanin dalilinta na cewa dan kasuwa Jimoh Ibrahim shine dan takarar Peoples Democratic Party a zaben gwamnan jihar Ondo da za'a yi ranar 26 ga Nuwamba.

KU KARANTA: Yanzu haka: Zanga-zanga mai girma ya tashi a jihar Ondo kan Jimoh Ibrahim (hotuna)

A cewar Olusegun Agbaje, kwamishinan zabe na jihar Ondo, INEC ta amince da zaman Ibrahim dan takarar PDP bisa ga dokar babbar kotun kasa dake Abuja wadda mai shari'a Okon Abang kema jagora a cewar rohoton Premium Times.

Mai shari'a Abang, ranar 14 ga Oktoba yace Ibrahim shine dan takarar PDP na gaskiya, ya kuma ki amincewa da rokon Eyitayo Jegede na a bashi damar daukaka shari'ar da aka yanke ranar  14 ga Oktoba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng