Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

A duk lokacin da zabe ya karato a Najeriya, yan siyasa kan yi amfani da salo daban daban don samun kuri’a daga jama’a. A daidai wannan lokaci ne yan siyasa zasu fara yinma yan kasa alkawurra daban daban.

Da yake cin zabe a Najeriya ya zama tamkar a-mutu-ko-ayi-rai, don haka ne yan siyasa ke yin duk mai yiwuwa don ganin sun dare kujerun da suke muradi. Sai kaga sun fara raba ma mutane buhunan shinkafa mai dauke da hotunan su, garri, doya, da dai sauran kayan abinci. Toh da yake akwai yunwa a tsakanin yan Najeriya, sai kaga mutane suna ta rubibin wadannan kayan abinci.

Yan Najeriya sun ma saba da samun irin kayayyakin nan a lokutan zabuka, ka wasu daga cikin ire iren abubuwan da yan siyasa ke rabawa a lokutan zabe.

1. Buhun Shinkafa

A gabanin zaben gwamnan jihar Ekiti a shekarar 2014, Gwamna Ayo Fayose ya raba shinkafa ga dalibai, mata yan kasuwa da ma’aikata. Dukkanin buhuhunan shinkafar na dauke da hotuna da sunan Fayose.

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

haka ma aka yi a zabukan 2015, inda jam’iyyar PDP ta raba buhunan shinkafa masu dauke da hotunan tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan

2. Buredi

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

Sanannen abu ne cewa tsohon shugaban kasa ya raba ma mutane Buredi yayin yakin neman zabe. Wai shin, idan ba’a Najeriya ba, a ina ne ake neman kuri’a da Buredi?

3. Littafin rubutu

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

A yayin zabukan shekarar 2015, jam’iyyar APC ta raba littafan rubutu wadanda suke dauke da hotunan dan takakar shugaban kasa Muhammad Buhari da dan takarar mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo a gaba, sai kuma manufofin jam’iyyar a bayan littafin.

4. Ashana

Jam’iyyun siyasa basu da dama, har da kwalin ashana suke rabarwa.

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

KU KARANTA: Buhari da Sultan na cikin musulmai mafi shahara a Duniya

5. Sabulu

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

Kodai jam’iyyun siyasa sun dauka yan Najeriya basa wanka ne? idan ba haka ba ya zasu rika raba mana sabulai? A nan ma jam’iyyar APC ce ta rabar da sabulu, wanda ake ganin gwamna Rochas Okorocha ne ya dauki nauyi.

6. Taliyar Noodle

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

Rahotannin sun tabbatar da PDP ta raba taliyar indomie na N50 yayin zabukan 2013.

7. Katin waya

Jam’iyyar APC c eta kirkiro salon rabon katin waya, inda tad aura hotunan ta a kan katukan kamfanin MTN.

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

8. Kosai

Kyaututtuka 8 da yan siyasa ke baiwa yan Najeriya

Nan bada dadewa ba aka samu wannan a jihar Edo gabanin zaben gwamnan jihar da ya gudana a ranar 28 ga watan satumba, inda wasu yayan jam’iyyar APC suka raba kosai kyauta a garin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng