Bayan rashin mataimakin gwamna, Jam’iyyar PDP za tayi rashin Yan majalisa 8 da jiga-jigai a Oyo

Bayan rashin mataimakin gwamna, Jam’iyyar PDP za tayi rashin Yan majalisa 8 da jiga-jigai a Oyo

Yan majalisar dokokin jihar Oyo takwas (8) na jam’iyyar People’s Democratic Party, PDP, da wasu jiga-jigan jam’iyyar a jihar na gab da sauya sheka jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

Daya daga cikin yan majalisar ta PDP, wanda ya bukaci a sakaye sunansa ya bayyana hakan ranar Lahadi a garin Ibadan, birnin jihar, rah rahoton Vanguard.

Ya laburta cewa suna shirin sauya sheka ne saboda jam’iyyar ta hanasu tikitin takara a zaben 2023.

Wannan lamarin ya biyo bayan sauya shekar da mataimakin Gwamnan jihar, Rauf Olaniyan, yayi daga PDP zuwa APC.

PDP ouo
Bayan rashin mataimakin gwamna, Jam’iyyar PDP za tayi rashin Yan majalisa 8 da jiga-jigai a Oyo
Asali: UGC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel