Watanni bayan mutuwar wani Mufti, Kyanwarsa taki tashi daga kan kabarinsa

Watanni bayan mutuwar wani Mufti, Kyanwarsa taki tashi daga kan kabarinsa

  • Hotunan wata kyanwa mai son maigidanta sun bazu a kafafen sada zumunta kuma mutane sun tofa albarkatun bakinsu
  • Sama da watanni biyu bayan mutuwar maigidanta, ta ki tashi daga kan kabarinsa saboda tsananin kewa
  • Mutane da dama sun bayyana mabanbantan ra'ayoyi kan halin da kyanwan ke ciki kuma ko tana cin abinci

Wani mutumi mai suna @LavBosniak a kafar sada zumunta ya bayyana yadda wata kyanwa taki barin kan kabarin maigidanta bayan watanni da mutuwarsa.

@LavBosniak ya laburta wannan ne ranar Talata, 9 ga Nuwamba, 2021.

Ya ce mamacin mai suna Mufti Muamer Zukorlić ya mutu ya lokacin rani amma har aka fara sanyi kyanwar ta ki rabuwa da shi.

Watanni bayan mutuwar wani Mufti, Kyanwarsa taki tashi daga kan kabarinsa
Watanni bayan mutuwar wani Mufti, Kyanwarsa taki tashi daga kan kabarinsa Hoto: @lavBosniak
Asali: UGC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Duk da Kyauna, “Samarin Shaho” Guduna Suke yi, Budurwa Mai Kamun Kai Tayi Bayani

Soyayya har bayan mutuwarsa

Hotunan sun nuna yadda kyanwar ke tsaye kan kabarin a zaune.

Mutane da dama sun bayyana cewa so da dama dabbobin da mutum ke kula da su da kyau sun fi son sa fiye da iyalansa da 'yayansa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel