Jerin jihohi 5 da suka fi aiwatarwa al'ummarsu manyan ayyuka na kasafin kudi, Kaduna ce ta farko

Jerin jihohi 5 da suka fi aiwatarwa al'ummarsu manyan ayyuka na kasafin kudi, Kaduna ce ta farko

Ayyukan da gwamnatocin jihohi da tarayya ke yiwa al'umma ya kasu kashi biyu; manya da sabbin ayyuka da kuma ayyukan yau da kullum.

A saukake, manyan ayyuka sune ayyukan da suka hada da hanyoyi, asibitoci, makarantu, dss.

Ayyukan yau da kullum kuwa sune albashi, fansho, alawus da da sauran su.

Tsakanin wadannan ayyuka, manyan ayyuka sun fi muhimmanci wajen cigaban tattalin arzikin jihar, a cewar BudgIT.

BudgIT tace: "Iya adadin kudin da gwamnati ta zuba cikin manyan ayyuka, iya irin ingantuwar tattalin arzikinta."

A sabon rahoton da BudgIT ta fitar, ta hararo jihohin da suka fi yiwa al'ummarsu manyan ayyukan da suka tsara a kasafin kudin 2019.

DUBA NAN: Wadanda suka yi garkuwa da dalibai a Kaduna sun fara kiran iyayen domin kudin fansa

Jerin jihohi 5 da suka fi aiwatarwa al'ummarsu manyan ayyuka na kasafin kudi, Kaduna ce ta farko
Jerin jihohi 5 da suka fi aiwatarwa al'ummarsu manyan ayyuka na kasafin kudi, Kaduna ce ta farko
Asali: UGC

KU KARANTA: Ba ni na raba shinkafa a Kano ba amma ina godiya ga wadanda sukayi, Tinubu

Ga jerin jihohi 5 mafi aiwatar da kasafin kudin 2019:

1. Jihar Kaduna

Kudin manyan ayyukan da aka kasafta : N152.3bn

Kudin da aka kashe kan manyan ayyuka: N148.3bn

Alkalamin aiwatarsa: 97.53%

2. Jihar Yobe

Kudin manyan ayyukan da aka kasafta : N39.5bn

Kudin da aka kashe kan manyan ayyuka: N30.1bn

Alkalamin aiwatarsa: 76.21%

3. Jihar Rivers

Kudin manyan ayyukan da aka kasafta : N301.5bn

Kudin da aka kashe kan manyan ayyuka: N224.1bn

Alkalamin aiwatarsa: 69.81%

4. Jihar Lagos

Kudin manyan ayyukan da aka kasafta : 345.3bn

Kudin da aka kashe kan manyan ayyuka: 241.1bn

Alkalamin aiwatarsa: 69.81%

5. Jihar Jigawa

Kudin manyan ayyukan da aka kasafta: 90.1bn

Kudin da aka kashe kan manyan ayyuka: 61.9bn

Alkalamin aiwatarsa: 67.99%

A bangare guda, Nyesom Wike, gwamnan jihar Ribas, ya ce duk wanda ke neman zama shugaban kasa a 2023 zai bukaci samun kuri'u a Ribas sannan ya hada kai da Kano ko Legas don samun nasara.

Jaridar The Nation ta rahoto cewa ya ce irin wannan gagarumar matsayar ce ta tabbatar da mahimmancin Ribas a cikin tsarin siyasar kasar nan, yana mai cewa babu wanda za a bari ya bata shi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel