Buhari ya tabbatar da tabarbarewar tattalin arziki da tsaro a Najeriya

Buhari ya tabbatar da tabarbarewar tattalin arziki da tsaro a Najeriya

- Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya sanar da cewa kasar nan tana cikin halin tabarbarewar tattalin arziki

- Ya kara da bayyana cewa, akwai manyan kalubale da kasar nan ke fuskanta na fannin tsaro a sassan kasar nan

- Shugaban kasar ya sanar da hakan ne a yayin jawabi ga 'yan Najeriya a ranar cikar kasar shekaru 60 da samun 'yancin kai

A ranar Alhamis, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mawuyacin hali a fannin tattalin arziki.

Ya ce hakan kuwa daidai yake da kowacce kasa domin kuwa dukkan duniya ne ake cikin wannan halin.

Buhari ya sanar da hakan ne a jawabinsa ga 'yan Najeriya a ranar da kasar ta cika shekaru 60 da samun 'yancin kai.

Shugaban kasar ya kara da amincewa da cewa, kasar na fuskantar matsalolin tsaro daban-daban a sassan kasar.

Ya ce, "A yau na tabbatar da cewa Najeriya tana cikin mawuyacin hali na tattalin azriki kuma hakan ce ta kasance ga kowacce kasa a fadin duniya. Muna fuskantar kalubalen tsaro a sassa daban-daban na kasar nan."

KU KARANTA: Mutum na farko da ya warke daga cutar HIV ya rasu sakamakon cutar Cancer

Buhari ya tabbatar da tabarbarewar tattalin arziki da tsaro a Najeriya
Buhari ya tabbatar da tabarbarewar tattalin arziki da tsaro a Najeriya. Hoto dag @Vanguard
Asali: Twitter

KU KARANTA: Fyade: Kotu ta kori soja daga aiki, ta yanke masa hukuncin shekaru 5 a gidan yari

A wani labari na daban, kungiyar Igbo for President Solidarity Congress (IPSC), wata kungiya ce a kudu maso yammacin Najeriya, ta tabbatar da bada hadin kai dari bisa dari akan shugabancin dan kudu maso gabas a shekarar 2023.

Ta ce yin hakan ne kadai zai kawo hadin kai a Najeriya. Shugaban kungiyar, Dr Olukayode OshinAriyo ne yayi wannan kiran a ranar Talata, 29 ga watan Satumba a Ibadan, jihar Oyo.

IPSC ta ce kamar yadda kundin tsarin mulkin 1999 ya nuna, kudu maso gabas suna da damar rike kujerar shugabancin kasar Najeriya.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel