Mutanen da cutar korona ta harba a Najeriya sun zarta dubu 30 - NCDC

Mutanen da cutar korona ta harba a Najeriya sun zarta dubu 30 - NCDC

Bayan fiye da watanni hudu kenan da bullar cutar korona karo na farko a Najeriya, cutar mai toshe kafofin numfashi ta yadu a jihohi 36 da kuma babban babban birnin kasar na Tarayya wato Abuja.

Wannan ya na kunshe cikin kididdigar alkaluman da Hukumar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa a Najeriya NCDC ta fitar a daren ranar Laraba, 8 ga watan Yuli.

Taskar bayanai ta NCDC ta nuna cewa, babu jihar da ba a samu bullar cutar ba a duk fadin kasar, inda a baya bayan nan aka gano masu dauke da kwayoyin cutar karo na farko a jihar Cross River.

A yayin da likafar cutar ke ci gaba babu sassauci, har yanzu jihar Legas ce ke jan ragama ta yawan masu cutar inda ta harbi mutum 11,670 sai kuma mutum 1,701 da suka warke, yayin da mutum 133 suka kwanta dama.

Kawo yanzu a duk fadin Najeriya, cutar ta harbi mutum 30,249, sai kuma mutum 12,373 da aka sallama daga cibiyoyin killace masu cutar bayan samun waraka, yayin da mutum 684 suka riga mu gidan gaskiya.

Shugaban NCDC; Chikwe Ihekweazu
Shugaban NCDC; Chikwe Ihekweazu
Asali: Twitter

Rumbun tattaro bayanai na NCDC ya nuna cewa, an yi wa mutum 171,931 gwajin cutar a duk fadin kasar tun bayan bullarta karo na farko a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Haka kuma alkaluman Cibiyar dakile cututtuka ta kasar sun nuna cewa, mutum 17,192 ne suka rage masu dauke da kwayoyin cutar.

Da misalin karfe 11.53 na ranar Laraba da daddare, NCDC ta sanar da cewa an gano karin sabbin mutane 460 da cutar ta harba a fadin Najeriya.

KARANTA KUMA: Jami'in ɗan sanda ya harbe ɗan kabu-kabu saboda rashin sanya takunkumin rufe fuska a Imo

Sabbin mutane 460 da cutar ta harba cikin jihohi 21 sun kasance kamar haka: Lagos (150); Rivers (49); Oyo (43); Delta (38); Abuja (26); Anambra (20); Kano (20); Filato (18); Edo (14); Bayelsa (13); Enugu (13); Osun (12); Kwara (10); Borno (8); Ogun (7); Kaduna (6); Imo (4); Bauchi (3); Gombe (3); Neja (2); Adamawa (1).

Baya ga jihar Legas da ta ke kan sahu na gaba ta fuskar yawan mutanen da cutar ta harba, birnin Abuja ya biyo bayanta a mataki na biyu da mutum 2,348 yayin da jihar Oyo ta biyo bayansu a mataki na uku da mutum 1,573.

Ga jerin adadin mutanen da cutar ta harba cikin kowace daya daga cikin jihohi 36 na Najeriya da cutar ta bulla:

Legas - 11,670

Abuja - 2,348

Oyo - 1,573

Edo - 1,503

Delta - 1,323

Kano - 1,291

Ribas - 1,284

Ogun - 1,057

Kaduna - 889

Katsina - 628

Borno - 563

Ondo - 550

Gombe - 524

Bauchi - 519

Ebonyi - 503

Filato - 478

Enugu - 431

Abia - 400

Imo - 356

Jigawa - 318

Kwara - 307

Bayelsa - 282

Nasarawa - 234

Osun - 210

Sokoto - 153

Niger - 124

Benuwe - 121

Akwa Ibom - 112

Adamawa - 100

Anambra - 93

Kebbi - 86

Zamfara - 76

Yobe - 61

Ekiti - 45

Taraba - 27

Cross River - 5

Kogi - 5

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel