Labarin gimbiyar da ta bar masarautarsu ta auri talaka ya dauki hankalin jama'a

Labarin gimbiyar da ta bar masarautarsu ta auri talaka ya dauki hankalin jama'a

  • Wata gimbiya ta yi watsi da dukkan jin dadin gidan sarauta ta auri wani talaka gama-gari
  • Wannan na zuwa ne bayan haduwarsu a shekarar 2012 a makaranta, lamarin mai ban sha'awa
  • Jama'a sun yi martani kan masoyan, inda Legit.ng ta tattaro muku maganar jama'a kan batun

Aljazeera ta ruwaito cewa za a daura auren gimbiya Mako ta kasar Japan da wani talaka mai suna Kei Komuro a watan Oktoba na 2021.

A baya kada, an lura cewa ma'auratan sun yi ta yawo a kafafen yanar gizo kwanaki da suka gabata bayan dangantakar su ta zama sananniya ga jama'a.

Labarin gimbiyar da ta bar masarautarsu ta auri talaka ya dauki hankalin jama'a
Gimbiya da masoyinta | Hoto: japantimes.com
Asali: UGC

Ta bar sarautarta saboda talaka

Domin ta auri mutumin da kowa yasan gama-gari ne kuma talaka, gimbiyar za ta ba da matsayin sarauta da gadon ta da ya kai biliyoyin kudade.

Kara karanta wannan

Ko a jikina asarar da na tafka, abu daya ne ya dame ni, Zuckerberg mai kamfanin Facebook

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A wani faifan bidiyo da Aljazeera ta yada, ma'auratan sun hadu da juna ne a shekarar 2012. An ce Komuro wanda lauya ne da ake fafatawa dashi a kasar Amurka.

Yadda suka shirya aurensu

An soke shirin ma’auratan na yin aure a shekarar 2018 bayan rahotanni da aka samu sun ce dangin angon na fuskantar matsalar kudi.

Ko da yake a kasar Japan ana tube mace daga sarautarta lokacin da ta bukaci auren talaka, hakan bai shafi maza ba. Rashin samun isassun maza a cikin iyali yana haifar da rikicin maye gurbinsu.

Martanin jama'a

Legit.ng ta tattaro martani kan yadda jama'a suka ji game da wannan labarin soyayya a kafafen sada zumunta.

inakablues ya ce:

"Yayi mata kyau ... ki fita yayin da zaki iya!"

surmeydee ya ce:

"Girmama ... kamar almara ... soyayya tayi nasara."

Kara karanta wannan

Babbar Magana: Sanata na goyon bayan IPOB, ya ce akwai kungiyoyin aware a kudu sun fi 30

tayatanzy ya ce:

"Kenan muna da Gimbiya 2 a Amurka yanzu."

marilyne_13 ya ce:

"Wannan ya wartsakar da zuciyata, ya ruda ni kuma ya girgiza ni gaba daya. Dokin soyayya ne ya dauke su .. wannan abin dariya ne."

daidaiedevereaux ya ce:

"Barka da zuwa kasarmu, Gimbiya. Inda mata ke yin duk abin da muke so (kawai ku guji Texas)."

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel