Abubuwa 7 da Shugaba Buhari ya fada a jawabin da yayi a majalisar dinkin duniya

Abubuwa 7 da Shugaba Buhari ya fada a jawabin da yayi a majalisar dinkin duniya

A ranar Juma'a, 24 ga Satumba, Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar da jawabi gaban shugabannin duniya a taron gangamin majalisar dinkin duniya UNGA76 dake gudana yanzu haka a birnin New York dake Amurka.

Buhari ya yi magana kan yada za'a farfado daga annobar COVID-19, sauyin yanayi, kare hakkin mutane da sauran su.

1. COVID-19

Shugaba Buhari ya gidewa duniya bisa matakin da suka dauka wajen dakile cutar COVID-19.

Ya bayyanawa duniya cewa gwamnatinsa na iyakan kokari wajen dakile cutar kan yan Najeriya.

2. Safara Makamai

Shugaba Buhari ya bayyana alhininsa kan yadda ake kasuwancin makamai ba bisa doka da tsari ba.

Kara karanta wannan

Ina karatu na tsawon awanni 17 a rana, Cewar matashin da ya gama Jami'a da 1st Class

A cewarsa, yada ake safara miyagun makamai na da illa ga rayuwa da tattalin arzikin kasashen Afrika.

3. Ta'addanci

Shugaban Najeriyan ya bayyana cewa gwamnatinsa zata cigaba da hada dai da hukumomin yaki da ta'addanci na majalisar dinkin duniya saboda yadda lamari ke tsamari a fadin duniya.

Ya bayyana cewa an nakasa kungiyar Boko Haram a Najeriya amma har yanzu suna kai hare-hare.

Abubuwa 7 da Shugaba Buhari ya fada a jawabin da yayi a majalisar dinkin duniya
Abubuwa 7 da Shugaba Buhari ya fada a jawabin da yayi a majalisar dinkin duniya Hoto: Buhari Sallau
Asali: Facebook

4. Sauyin Yanayi

Buhari ya bayyana illar sauyin yanayi kan Najeriya, inda yace an fari ganin illar hakan a bushewar tekuna, gudun hijra da kuma rashin abinci.

5. Dukiyoyin sata

A jawabin da ya gabatar, shugaban kasan yace kokarin da sukayi na kwato kudaden sata da wasu suka boye a kasashen waje ya taimaka wajen samun kudaden amfani lokacin yaki da annobar Korona.

6. Rashawa

Ya kara da cewa har ila yau Rashawa na da mumunan illa gazaman lafiya da tattalin arziki, musamman a kasashe masu tasowa irin Najeriya.

Kara karanta wannan

Bamu kujeran shugaban kasa a 2023 ya zama wajibi, Afenifere ta jaddada bukatar kudu

7. Kare hakkin dan Adam

Shugaban Najeriyan ya bayyana cewa kasarsa ba zata yi kasa a gwiwa wajen cigaba da kare hakkin dan Adam ba.

Shugaba Buhari ya tafi New York don halartar taron UNGA a ranar Lahadi

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja a ranar Lahadi, 19 ga watan Satumba zuwa birnin New York a Amurka.

Legit.ng ta rahoto cewa shugaban kasar zai halarci taro na 76 na babban zauren Majalisar Dinkin Duniya (UNGA76). An bude taron ne a ranar Talata, 14 ga watan Satumba

Asali: Legit.ng

Online view pixel