Sheikh Gumi na karfafa fashi da makami a arewa, Kungiyar CAN ta yi zargi

Sheikh Gumi na karfafa fashi da makami a arewa, Kungiyar CAN ta yi zargi

  • Kungiyar CAN ta zargi shahararren malamin Musulunci, Sheikh Ahmed Gumi, da karfafa ayyukan fashi da makami a yakin arewa
  • Shugaban kungiyar reshen jihar Imo, Rev. Eches Divine Eches, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai
  • Ya ce matsaalar rashin tsaro da ke tasowa a arewa na iya cinye kasar baki daya idan har gwamnati ba ta dauki matakan da suka dace ba

Imo - Kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) ta zargi malamin addinin Islama, Sheikh Ahmed Gumi, da karfafa gwiwar 'yan bindiga da ayyukan su a arewacin Najeriya, jaridar Sun ta ruwaito.

Shugaban CAN na jihar Imo, Rev. Eches Divine Eches, ya bayyana hakan a cikin wata hira da ya yi da manema labarai a Abuja gabanin bikin cikar sa shekaru 45 da ranar da aka kafa sa a Owerri, jihar Imo.

Kara karanta wannan

Gwamna Matawalle ya sanar da dalilin da yasa suka daina sasanci da 'yan bindiga

Sheikh Gumi na karfafa fashi da makami a arewa, Kungiyar CAN ta yi zargi
Sheikh Gumi na karfafa fashi da makami a arewa, Kungiyar CAN ta yi zargi Hoto: Daily Trust
Asali: Facebook

Ya yi hasashen cewa rashin tsaro da ke tasowa a arewa na iya cinye kasar baki daya tunda gwamnati ba ta duba ayyukan 'yan bindiga da ke tayar da hankulan jama'a da gaskiya.

Don haka, ya shawarci gwamnati da ta gargadi ga Sheikh Gumi, wanda ya yi iƙirarin cewa kalamansa, ya ƙarfafa gwiwar ‘yan ta'adda, ta haka, yake kara inganta ayyukan su na rashin imani a yankin arewa.

Jaridar Vanguard ta kuma ruwaito faston ya ci gaba da cewa sai dai idan an dauki tsauraran matakai don dakile lamarin almajirai, idan ba haka ba fashi da makami zai ci gaba da zama a arewa na dogon lokaci tare da yin illa ga rayuwar zamantakewa da tattalin arziki.

Ya ce:

“Ba zai yiwu ku kasance da tsarin rayuwar Almajiranci da gwamnati ba a cikin shekaru 40 da suka gabata a cikin al’ummarmu da ke tarbiyyantar da mutane ba tare da wata alama ga iyalai, garuruwa ko ƙasashen su ba. Waɗannan yaran suna warwatse a ko'ina a kan tituna ba tare da kun san cewa wata rana za su bar titi sannan su tafi daji inda za su fara yin sana'ar garkuwa da mutane ba.

Kara karanta wannan

Abinda yasa na bar PDP, gwamnonin PDP 3 da na sha alwashin ja zuwa APC, Fani Kayode

"Hakanan, a cikin al'umma mai hankali ba za ku iya samun irin su Sheikh Gumi ba, malamin addini da ke habbaka ta'addanci kuma ku yi tunanin hakan zai ci gaba. Duk da haka, shine abin da muke gani a yau. Ba ma ganin wani abu fiye da abin da muka shuka.

“Mun bar wannan abu (rashin tsaro) ya ci gaba kuma yanzu zai cinye kasar, idan ba a dauki tsauraran matakan fitar da su (Almajiri) daga kan tituna ba. A ba su damar mallakar hankalin kansu, a sanya su a makaranta, kuma taimaka musu su fahimci damar su.

“Barayin nan su ne Almajiri wadanda a da suke gaban gidajen mu suna bara. Duk da haka, muna addu’a kuma wannan shine dalilin da yasa har yanzu Allah ke raya al’ummarmu. Na yi imani Allah zai ci gaba da tallafa mana da sunan Yesu.”

'Yan bindiga sun sanar min salon da suke bi wurin guje wa luguden sojin sama, Gumi

Kara karanta wannan

Shugaban EFCC ya yanki jiki ya fadi yayin da yake magana a dakin taro

A wani labarin, sanannen malamin addinin Islama mazaunin Kaduna, ya kara tabbatar wa da jama'a cewa a koda yasuhe ya na samun damar tattaunawa da 'yan fashin dajin da suka addabi arewacin Najeriya.

A takardar da malamin ya fitar a cikin kwanakin nan, ya bayyana cewa gungun 'yan bindiga sun sanar da shi cewa luguden ruwan wutan da sojin saman ke yi ba ya taba su, sai dai ya taba matansu da 'ya'yansu, domin kuwa suna da salon kauce musu, Punch ta ruwaito.

Gumi ya ce 'yan bindigan sun kware tare da zama 'yan hannu wurin kauce wa duk wani bam da sojin sama za su wurgo, hakan ne yasa da kyar a iya kama su ko halaka su.

Asali: Legit.ng

Online view pixel